Majalisar Dinkin Duniya ta kaddamar shirin kawar da fatara a cikin shekaru 15 masu zuwa
A jiya mahukumtan kasashen duniya sun amince da wani shirin Majalisar Dinkin Duniya da zai inganta ci gaba a duniya a cikin shekaru 15 masu zuwa, a fannonin da suka shafi Ilimi, yakin da talauci, kiyon lafiya, da kuma matsalar dumamar yanayi.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
A lokacin buda taron da ya hada shuwagabanin kasashen duniya 150 a zauren Majalisar Dinkin Duniya (MDD) dake birnin New York, inda za suka tsaida bukatar cimma jerin muradun 17, domin samar da ci gaba mai dorewa ga duniya nan da karshen ta 2030,
Wannan dai wani sabon shiri ne da zai canji shirin cimma muradun karni Majalisar Dinkin Duniya (MDD) na cimma muradun karni a cikin shekaru 15 da suka gabata a wannan shekara ta 2015 da muke ciki
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu