Faransa da Birtaniya za su karbi ‘Yan gudun hijirar Syria
Shugaban Faransa Francois Hollande ya ce kasarsa za ta karbi ‘Yan gudun hijira kimanin 24,000 cikin shekaru biyu, tare da yin kiran gudanar da babban taro kan matsalar bakin haure da ke ci gaba da kwarara zuwa kasashen Turai.
Wallafawa ranar:
Kungiyar Tarayyar Turai ta bayyana matsalar bakin-haure a matsayin mafi muni tun yakin duniya na biyu.
Birtaniya ma ta amince ta karbi ‘Yan gudun Hijirar Syria kimanin 20,000 a cikin shekaru biyar daga sansaninsu a kasashen Lebanon da Turkiya da Jordan.
Tun da farko Jamus ta bayyana matakin karbar bakin haure 31,400. Kasar ta amince da matakin ne don rage wa kasashen Girka da Italiya da hungary nauyin hidimar bakin hauren.
Shugaba Hollande ya yi gargadi akan daukar matakan da suka dace kan raba bakin hauren tsakanin mambobin kasashen Turai.
Shugaban ya ce nan gaba zai jagoranci taro na musamman kan matsalar bakin haure a Paris.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu