Isa ga babban shafi
Transparency

Transparency ta fitar da sabon rahoto kan rashawa a duniya

Rahoton da kungiyar yaki da rashawa ta duniya Transparency International ta fitar, ya bayyana kasashen Afghanistan, Koriya ta Arewa da kuma Somaliya a matsayin kasashen da rashawa ta fi yaduwa, yayin da rahoton ke cewa kasashen Denmark da kuma New Zealand ne suka fi kokari wajen kawar da matsalar. 

Alamar kungiyar Transparency
Alamar kungiyar Transparency RFI/Persan
Talla

Rahoton ya ce kashi 70 cikin dari na kasashen duniya ne ke fama da rashawa, kuma a cikin ma’aikatun gwamnati ne matsalar ta fi yin kamari, tare da nuna yatsa a kan jam’iyyun siyasa, ‘yan sanda, alkalan kotu da dai sauransu.

Har ila yau binciken da kungiyar da ke da mazauni a birnin Berlin na kasar Jamus ta fitar, ya bayyana cewa kasashen da ke fama da tashe-tashen hankula kamar Syria, Mali da kuma Libya, sun samu koma baya a fagen yaki da rashawa.

To sai dai sakamakon komawa a kan turbar dimokuradiyya, kasashe da dama ne ke ci gaba da kokarin kawar da matsalar kamar Najeriya da kuma Myanmar a cewar Transparency International.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.