Ecuador
Gwamnatin Ecuador ta bukaci ‘Yan Jarida biyan kudade
Wata Kotu a kaasr Ecuador, ta bukaci wasu ‘Yan Jaridu biyu biyan shugaban kasa, Rafael Correa, Dala miliyan daya kowannensu, saboda bata masa suna akan zargin da suka yi masa na bai wa Dan uwansa kwangilar makudan kudade.
Wallafawa ranar:
Talla
‘Yan Jaridun biyu sun yi zargin ne a rahotan da suka wallafa, yayin da shugaban kasar yace, bashi da labarain cewar an bai wa Dan uwansa kwangilar Dala miliyan 167.
Bayan jin labarin ne shugaban ya soke kwangilar.
Shugaban kasar yace, bai gamsu da hukuncin kotun ba, saboda kudin tarar sun yi kadan, saboda haka zai daukaka kara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu