Isa ga babban shafi

Adadin wadanda suka mutu a girgizar kasar Indonesia ya kai 252 a yanzu

Masu aikin ceto sun yi ta aikin lalubo wadanda suka saura da ransu a karkashin baraguzan gine gine a yayin da ‘yan uwa da abokai suka fara jana’izar masoyansu da suka mutu bayan girgizar kasar da ta lakume rayuka 252 a Tsibirin Java na kasar Indonesia.

Masu aikin ceto suna kwashe wadanda suka ji rauni bayan girgizar kasa a Cianjur, na kasar Indonesia.  21 ga Nuwamba 2022.
Masu aikin ceto suna kwashe wadanda suka ji rauni bayan girgizar kasa a Cianjur, na kasar Indonesia. 21 ga Nuwamba 2022. via REUTERS - ANTARA FOTO
Talla

A yayin da ake ci gaba da zakulo matattu, hankali ya karkata ga wadanda ake tunanin suna da ransu, wadanda har yanzu ke karkashin baraguzai.

Inda wannan girgizar kasar da ta kai maki 5 da digo 6 ta fi yin tasiri  shine garin Cianjur, indaa aaka fi samun akasarin wadanda suka mutu, kuma daruruwa suka jikkata a yayin da ake fargabar gwammai suna makale a cikin baraguzan gine ginen da da inda aka samu zaftarewar kasa.

A Talatar na ne adadin wadanda suka mutu a wannan iftila’in ya tashi zuwa 252 daga 162 tun da farko, kamar yadda wani kakakin gwamnati a. Cianjur ya baayyana.

A yau Talata shugaba Joko Widodo ya ziyarci yankin da lamarin ya auku, inda ya bada gudummawa ga wadanda abin ya shafa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.