Isa ga babban shafi
Iran-Nukiliya

Ana daf da farfado da tattaunawar yarjejeniyar nukuliyar Iran

A jiya Asabar Iran da hukumar kula da makamashin nukkiliya ta duniya suka ce sun amince su bi hanyoyin warware matsalolin da ke wa yarjejeniyar nukiliyar 2015 kafar ungulu.

Shugaban hukumar makamashin nukiliya ta duniya Rafael Gross,  Mohammad Eslami, a birnin Tehran.
Shugaban hukumar makamashin nukiliya ta duniya Rafael Gross, Mohammad Eslami, a birnin Tehran. via REUTERS - WANA NEWS AGENCY
Talla

Sanarwar na zuwa ne bayan da Rasha ta ce za ta nemi tabbaci daga Amurka kafin ta goyi bayan yarjejeniyar, lamarin da ke bada kwarin gwiwar cewa za a cimma yarjejeniya.

Shugaban hukumar makamashin nukiliyar, Rafael Grossi ya ce akwai ababe da dama da ya kamata a warware, amma hukumar ta yanke shawarar yin mai yiwuwa.

Shugaban hukumar makamashin nukiliya a Iran, Mohammed Eslami  ya ce lallai bangarorin biyu sun cimma matsayar cewa za su yi musayar wasu kundaye a tsakaninsu nan da 22 ga watan Mayu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.