Isa ga babban shafi
Isra'ila-Falasdinawa

Isra'ila ta sake kama fursunoni Falasdinawa da suka tsere daga gidan yarinta

‘Yan sanda  a Isra’ila sun ce sun kama 4 daga cikin fursunoni 6 da suka tsere daga wani gidan yari mai cike da matakan tsaro a farkon wannan mako.

Hoton da 'yan sandan Isra'ila suka saki, wanda ke nuna Zakaria Zubeidi (hagu) da Mohammad Ardah fuskarsu a rufe bayan an sake kama su.
Hoton da 'yan sandan Isra'ila suka saki, wanda ke nuna Zakaria Zubeidi (hagu) da Mohammad Ardah fuskarsu a rufe bayan an sake kama su. - ISRAELI POLICE/AFP
Talla

Tun bayan tserewar da fursunonin suka yi a ranar Litinin ne rundunar sojin kasar ta baza dakaru a sassan kasar da zummar sake damko  su.

Fursunoni 2 da aka sake kamewa a baya bayan nan, wadanda aka same su boye  a wata tashar manyan motoci a arewacin Nazareth sun hada da wani fitaccen jagoran ‘yan tsagera.

Zakaria Zubeidi, mai shekaru 45, tsohon jagora ne na mau fafutuka a kungiyar Fatah ta shugaban Falasdinawa Mahmud Abbas a birnin Jenin, kuma yana cikin wadanda aka sake kamawa bayan sun tsere.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.