Iran ta ci gaba da shirinta na sarrafa makamashin Uranium
Iran ta sanar da ci gaban shirinta na inganta makamashin Uranium a wani matakin da ya saba wa yarjejeniyar nukiliya ta shekarar 2015 da ke cikin rudani, kwanaki bayan da aka fara aka tattaunawa kan ceto yarjejeniyar.
Wallafawa ranar:
Shugaba Hassan Rouhani a hukumance ya kaddamar da Shirin a wani biki da aka watsa kai tsaye da gidan talabijin din kasar.
Matakin na baya-bayan nan da Iran ta dauka na kara inganta uranium ya biyo bayan bude zagayen tattaunawar ranar Talata tare da wakilan sauran bangarorin da suka rage a yarjejeniyar nukiliyar kan dawo da Amurka cikin ta.
Tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya fice daga yarjejeniyar a shekarar 2018.
Iran dai ta bukaci janye takunkuman da tsohon shugaban Amurka Donald Trump ya kakkaba mata a shekarar 2018, domin komawa mutunta yarjejeniyar nukiliyar ta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu