Isa ga babban shafi
Pakistan-India

Pakistan ta gargadi MDD kan kazancewar rikicinta da Indiya

Fira Ministan Pakistan Imran Khan ya gargadi majalisar dinkin duniya da cewar rikicin dake tsakaninsu da Indiya kan yankin Kashmir, ka iya kazancewa zuwa barkewar yaki da makaman nukiliya, abinda ba zai yiwa duniya dadi ba.

Fira Ministan Pakistan Imran Khan yayin jawabi a zauren majalisar dinkin duniya. 27 ga Satumba, 2019.
Fira Ministan Pakistan Imran Khan yayin jawabi a zauren majalisar dinkin duniya. 27 ga Satumba, 2019. REUTERS/Lucas Jackson
Talla

Imran Khan ya yi gargadin ne a lokacin jawabi a zauren majalisar dinkin duniya, dake ci gaba da taron ta kashi na 74.

Fira Ministan na Pakistan yace yanzu haka India ta jibge jami’an tsaro dubu 900,000, a yankin Kashmir mai rinjayen Musulmi dake karkashinta, matakin da ake ganin zai sa su arangama da mutanen Yankin wadanda ke cikin ukubar rashin walwala yanzu haka.

Rikici ya so barkewa a yankin na Kashmir ne, bayan da Indiya ta soke kwarya-kwaryar ‘yancin da yankin na Kashmir dake karkashin ta ke da shi, bisa zargin cewa Pakistan kan amfani da yankin wajen kaddamar da ayyukan ta’addanci a Indiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.