Turkiya ta musanta bude wuta kan 'yan gudun hijirar Syria
Turkiya ta musanta cewa sojojinta suna bude wuta kan ‘yan gudun hijira da ke neman ketarawa cikin kasar daga Syria.
Wallafawa ranar:
Kungiyar kare hakkin dan adam ta Human Rights watch ce ta fara fitar da rahoton a jiya Asabar, wanda ya ce dakarun Turkiya sun shafawa idanunsu toka wajen hallaka masu neman mafakar daga Syria, da ke gujewa yakin da ake gwabzawa a lardin Idlib.
Sai dai gwamnatin Turkiya ta musanta hakan, tare da jaddada cewa tun bayan barkewar yakin basasar kasar ta Syria a 2011 zuwa yanzu, Turkiyan ta bai wa ‘yan gudun hijirar Syria akalla miliyan uku da dubu dari biyar mafaka.
Hukumar kare hakkin dan adam ta 'Human Rights Watch' ta ce daga ranar 15 ga watan Disamba na shekarar 2017 zuwa 15 ga watan Janairu da ya gabata, akalla 'yan kasar Syria dubu 247 ne suka tsere zuwa yankunan da ke kan iyakar Syria da Turkiya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu