Hariri ya bayyana janye murabus din da ya yi
Firaministan Lebanon Saad Hariri ya bayyana janye murabus din da ya yi wata guda da ya gabata, bayan wani taron Majalisar ministocin kasar yau talata.
Wallafawa ranar:
Majalisar ministocin ta bayyana farin cikin ta da matakin, kana kuma ta bayyana matsayin ta na zama ‘yar baruwan mu daga duk wani rikicin da ya shafi kasashen larabawa.
Ana saran Hariri ya ziyarci birnin Paris na Faransa ranar juma’a domin halartar wani taro da za’a yi kan murabus din da ya yi, wanda zai samu halartar Sakataren harkokin wajen Amurka Rex Tillerson.
Murabus din Hariri ya haifar da furgaban barkewar sabon rikicin siyasa da tattalin arziki a kasar da ke fama da rabuwar kawuna.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu