Isa ga babban shafi
Iran

Iran ta yi barazanar kara nisan zangon makamanta masu linzami

Rundunar sojin juyin juya halin kasar Iran ta yi gargadin cewa zata kara karfi da kuma nisan zangon manyan makamai masu linzamin da ta ke kerawa, da akalla kilo mita 2,000, muddin ta fuskanci wata barazana daga nahiyar turai.

Sabon makami mai linzami da kasar Iran ta kera, wanda ake sarrafa shi da na'urar komfuta. An gwada wannan makami a wani wuri da aka sakaya a ranar 11 ga Oktoban 2015.
Sabon makami mai linzami da kasar Iran ta kera, wanda ake sarrafa shi da na'urar komfuta. An gwada wannan makami a wani wuri da aka sakaya a ranar 11 ga Oktoban 2015. REUTERS/farsnews.com
Talla

Gargadin na Iran ya zo ne bayan da kasar Faransa ta bukaci, nahiyar turai ta sake tattaunawa da Iran kan shirinta na kera manyan makai masu linzami, domin cimma yarjejeniya, bayan wadda aka cimma da kasar kan shirinta na inganta makamashin nukiliya a 2015.

Sai dai Iran ta ce tana kera manyan makamai masu linzamin ne domin kare kanta kawai, dan haka ba zata amince da duk wani yunkurin kasashen turai ba cimma yarjejeniya da ita, don ta dakatar da shirin.

A watan da ya gabata ne shugaban rundunar sojin juya juya halin Iran, Muhammad Ali Jafari, ya ce iran ta mallaki manyan makamai masu linzami da zasu iya tafiyar kilo mita 2000, abinda ke nufin zata iya amfani da su kan duk wata barazanar sojin Amurka a yankin gabas ta tsakiya, dan haka babu bukatar sai sun kara karfin nisan tafiyar da makaman zasu yi.

Iran na kan gaba a tsakanin kasashen da suka mallaki karfin manyan makamai masu linzami a gabas ta tsakiya, wanda zasu iya kai hari da su kai tsaye, kan kasar Isra’ila.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.