Isa ga babban shafi
Najeriya

Tarayyar Turai ta karfafa takunkumi akan Koriya ta Arewa

Kungiyar Tarayyar Turai ta kara zafafa takunkumin da ta malkayawa kasar Koriya ta arewa saboda ayyukan Nukiliya da gwaje gwajenta na makamai masu linzami

Koriya ta Arewa ta yi gwajin makamai sau 12
Koriya ta Arewa ta yi gwajin makamai sau 12 REUTERS
Talla

Kungiyar ta fadi cewa za ta rufe asusu da kadarori na wasu mutane akalla 14 da hana su tsoma kafarsu a Turai kamar yadda Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya nemi a yi makon jiya, kan karfafa wa Koriya takunkumi kan gwajin makaman da kasar ke yi masu hadari.

Kungiyar Tarayyar Turai ta kuma malkaya wa wasu kamfanonin Koriya takunkumi.

Zuwa yanzu mutane 94 ‘yan kasar Koriya ta Arewa takunkumin Tarayyar Turai ya shafa, da kamfanoni 53.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.