Guguwa ta hallaka mutane a Philippines
Akalla mutane hudu ne aka tabbatar da mutuwarsu sakamakon wata guguwa mai dauke da ruwan sama da ke gudun sama da kilomita 230 a cikin awa guda da ta afka wa kasar Philippines.
Wallafawa ranar:
Guguwar wadda aka yi wa lakabi da Nock-Ten, ta haddasa barna ta hanyar kwashe gidaje da kuma lalata turakan wutar lantarki.
Sama da mutane dubu 218 ne aka kwashe, yayin da aka soke tashi da saukar jiragen sama gabanin aukuwar guguwar.
Philippines dai kasa ce da ta saba fuskantar irin wannan guguwa mai karfi tare da ruwan sama, in da a shekara ta 2014, wata guguwa ta yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da dubu 7.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu