Syria
A na ci gaba da ruwan wuta a birnin Aleppo
Jiragen Yakin Gwamnatin Syria da na Rasha na ci gaba da ruwan wuta kan birnin Aleppo, inda kayayyakin abincin agaji da ake bayar wa yake gab da karewa.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahotannin sun ce a cikin sa’o'i 24 an ruwaito cewar akalla mutane 35 aka kashe a birnin, matakin da ya harzuka Amurka da Majalisar Dinkin Duniya.
Kungiyar da ke sa ido kan rikicin kasar ta ce cikin wadanda aka kashe harda yara kanana guda 6.
Kungiyar likitoci masu zaman kan su ta ce cikin wuraren da aka kai hari harda wasu cibiyoyin kula da lafiya guda biyu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu