Isa ga babban shafi
IRAKI

ISIL za ta ci gaba da fafutuka don rike birnin Mosul

Shugaban Kungiyar ISIL Abubakar al-Baghdadi ya bukaci mayakan sa dake Mosul da kar su bada kai bori ya hau a fafatawar da suke wajen ci gaba da iko da garin.

Shugaban kungiyar ISIL mai da'awar jihadi Abakr al-Baghdadi.
Shugaban kungiyar ISIL mai da'awar jihadi Abakr al-Baghdadi. REUTERS/Social Media Website via Reuters TV
Talla

Shugaban ya bayyana hakan ne  a wani sakon da ya aika ta intanet, inda yake shaida musu cewar ci gaba da tirjiya wajen kare garin shine mafi alkhairi a gare su.

Baghdadi ya gargadi mayakan da su kare kasar su wajen yakar mayakan dake neman raba su da garin.

Babban birnin Mosul wadda shine gari na biyu mafi girma a kasar Iraki ya fada hannun kungiyar ISIL shekaru biyu da suka gabata kafin yanzu gwamnati kasar ta yunkuro da shirin sake karbe birnin.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.