Isa ga babban shafi
Philippines

Kungiyar Yahudawa ta bukaci shugaban Philippines ya nemi afuwarta

Kungiyar Yahudawa ta Duniya yi kakkausar suka ga kalaman shugaban Philippines Rodrigo Duterte, wanda ya kamanta yakin da yake da masu tu’ammuli da miyagun kwayoyi a kasarsa da kisan kare dangin da Gwamnatin Nazi karkashin Adolf Hitlar ta yiwa Yahudawa.

Shugaban kasar Philippines Rodrigo Duterte
Shugaban kasar Philippines Rodrigo Duterte Reuters
Talla

A baya Duterte ya furta kalaman cewa zai yi farin cikin zai kashe masu tu’ammali da muggan kwayoyi a kasar, kamar yadda Hitlar a kashe Yahudawa a lokacin mulkinsa a Jamus.

Shugaban kungiyar Yahudawa na Duniya Ronald S. Lauder, ya bukaci shugaban na Philippines ya janye kalamansa tare da neman afuwa.

Kawo yanzu dai sama da mutane 3000 aka kashe a Philippines wadanda aka zarga da ta’ammuli da muggan kwayoyi.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.