Isa ga babban shafi
Yemen

Fada ya ritsa da mutane 200,000 a Yemen

Majiyar Sojin kasar Yemen tace akalla mutane 40 suka mutu a fafatwar da akayi tsakanin Yan Tawayen Huthi da dakarun dake goyan bayan gwamnatin kasar, a garin Taez dake kudu maso yammacin kasar. 

Birnin Taiz da ke fama da rikici tsakanin sojin gwamnati da 'yan tawaye.
Birnin Taiz da ke fama da rikici tsakanin sojin gwamnati da 'yan tawaye. REUTERS/Anees Mahyoub
Talla

Kakakin sojin kasar Kanar Sadiq al-Hassani yace daga cikin mutanen da aka kasha, 27 ‘yan tawayen Huthi ne, kana 13 daga ciki sojojin gwamnati.

Har yanzu ana ci gaba da fafatawa tun bayan katsewar tattaunawar zaman lafiyar da akayi a kasar Kuwait.

Sama da fararen hula 200,000 ne fada ya ritsa da su a garin Taiz da ke tsakanin babban birnin kasar Yemen Sanaa da kuma birnin Aden.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.