Korea ta Arewa-Korea ta Kudu
Korea ta yi gwajin Makamin Nukiliya mafi girma
Shugabar Kasar Koriya ta Kudu Park Guen-Hye ta ce Koriya ta Arewa ta yi gwajin makami mafi girma a kasar wanda karfin sa ya kai maki kusan 5 da rabi, ya kuma razana Jama’a kamar karfin girgizar kasa.
Wallafawa ranar:
Talla
Gwajin na zuwa ne kwana guda bayan Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana shirin karawa kasar takunkumi saboda abinda ta kira karya ka’ida wajen gwajin makaman da ta ke yi.
Shugabar Koriya ta kudun ta ce za su ci gaba da daukan dukkan matakan da suka da ce wajen ladabtar da kasar cikin su harda takunkumin karya tattalin arziki.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu