Isa ga babban shafi
China

Kotu ta ba China rashin gaskiya akan Phillippines

Wata kotun duniya a Hague ta zartar da hukuncin da ya ba China rashin gaskiya kan takaddamar da kasar ke yi da Philippines na mallakar wani tsibiri da ke kan teku a kudancin China.

Masu Zanga-zangar adawa da China a Makati a Philippines
Masu Zanga-zangar adawa da China a Makati a Philippines REUTERS/Erik De Castro
Talla

A yayin da kotun ke yanke hukuncin ta ce China ta sabawa ‘yancin kasar Philippines akan mamayar yankin da ta ke yi.

A yau Talata ne kotun ta yanke hukuncin kan takaddamar game da mallakar tsibiran da ke kan teku a kudancin kasar China.

Kasar China ta ki halartar zaman kotun tare da yin watsi da hukuncin da kotun ta zartar a yau kamar yadda ta fitar da sanarwa bayan yanke hukuncin.

China ta ce ba a bata damar kare kanta ba a kotun kan ikirarin da ta ke na mallakar yankin tsibiran mai arziki.

Kasar Philippines ce ta gabatar da koken a gaban kotun ta Hague wacce kasashen biyu suka sanya hannun amincewa da kafa kotun a karkashin Majalisar Dinkin Duniya.

Tuni gwamnatin Philippines ta gargadi ‘yan kasarta da ke China da su yi taka-tsan-tsan don kaucewa duk wata barazana da kan iya tasowa bayan yanke hukuncin.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.