Masu zanga zanga 5 sun mutu a India
Mutane 5 aka tabbatar da mutuwarsu a arangama tsakanin masu zanga zanga da sojin gwamnati a yankin Kashmir sakamakon kisan da aka yiwa wani madugun adawa.
Wallafawa ranar:
Akalla mutane 23 ne suka mutu tun bayan soma zanga zangar a ranar juma’ar da ta gabata, a yayin da wasu daruruwa suka sami rauni, duk kuwa da dokar hana fita da gwamnati ta ayyana a yankin.
Yanzu haka ma dai al’ammura sun tsaya cak sanadiyar rikicin, wannan ya kasance tashin hankali mafi muni da yankin ke fuskanta tun shekarar 2010.
A ranar juma’ar da ta gabata ne aka soma zanga zangar bayan kisan da aka yiwa madugun adawa kuma jagoran kungiyar Hizbul Mujahideen na yankin Kashmir a arangamar da ta auku tsakanin magoyansa da dakarun gwamnati.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu