India
Mutane 17 sun mutu a cibiyar aje makami a India
Wata gobara da ta tashi a rumbun aje makaman sojin kasar India ta yi sanadiyar rasa rayukan mutane 17, yayin da wasu da dama suka samu raunuka.
Wallafawa ranar:
Talla
Kamfanin dillancin labaran kasar ya ce cikin mutane 17 da suka mutu sun hada da sojoji 2 a tashar Pulgaon da ke kusa da birnin Nagpur a Jihar Maharashtra.
Tuni aka kwashe dubban mutanen da ke zama a kauyukan dake kusa da tashar domin fargabar sake fashewar wasu abubuwa.
Rahotanni sun ce an yi kokarin kashe gobarar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu