Syria
Dakarun Syria sun kashe mayakan Al-Nusra
Dakarun gwamantin Syria sun kashe mayakan kungiyar Al-Nusra reshen kungiyar Al-Qaida a kasar akalla 19 a kusa da garin Allepo da ke arewacin kasar kamar dai yadda wata kungiya mai zaman kanta da ke sa-ido kan lamurran da ke faruwa a kasar ta sanar.
Wallafawa ranar:
Talla
Haka zalika sojojin na gwamnati sun harba bama-bamai akan wasu unguwannin da ke arewacin birnin tare da kashe mutane da dama ciki, har da fararen hula a cewar kungiyar ta OSDH mai ofishi a Birtaniya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu