Sojan Syria na ci gaba da nosawa zuwa garin Palmyra
Dakarun gwamnatin Syria da ke samun goyon bayan sojin saman Rasha na ci gaba da nosawa a cikin Palmyra domin fatattakar mayakan IS daga ciki wannan gari mai tarihi da ya share tsawon watanni a hannun kungiyar.
Wallafawa ranar:
Manema labarai da ke kan wani tsauni a gefen birnin na Palmyra, sun tabbatar da cewa sojin kasa na Syria na a kofar Palmyra, kuma kafin nan tuni suka karbe ikon ganin Amiriyah da ke kusa da shi.
IS dai na a matsayin kungiyar ‘yan ta’adda da ta fi tayar da hankalin duniya a wannan zamani, inda ake danganta hare-haren kungiyar da Hare-haren Brussels da kuma Paris a kan baraden kungiyar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu