Isa ga babban shafi
Syria

Mutane 500 sun mutu a Syria

A kasar Syria, mutane sama da 500 aka tabbatar da mutuwarsu a cikin wannan watan na Fabairu kadai, hakan kuwa ya faru ne sakamakon luguden wutan da dakarun gwamnatin kasar ke yi kan ‘yan tawaye tare da samun goyon bayan Rasha .

Birnin Aleppo na Syria na fama da hare hare
Birnin Aleppo na Syria na fama da hare hare Reuters/Hosam Katan
Talla

Hukumar da ke sa ido kan rikicin  Syria ta tabbatar da mutuwar mutane dari biyar da shida a yankin Aleppo, sakamakon munanan hare haren da  dakarun gwamnati suka kaddamar a mabuyar 'yan tawayen a farkon wannan watan.

Asarar rai da aka tafka ta kara haddasa matsalar tserewar dubban mutane daga kasar zuwa kan iyakar Turkiya, yayin da Turkiyan ta ki ba su damar shiga kasar saboda tana fama da 'yan gudun hijrar Syria sama da miliyan biyu a yanzu haka.

Hare haren Rasha a Syria dai na ci gaba da fuskantar suka daga wasu kasashen duniya  yayin da majalisar dinkin duniya ta yi kira ga Rasha da ta gaggauta kawo karshen hare harenta a Syria ganin asarar rayukan fararen hula da ake samu a duk lokacin da ta yi luguden wuta da zummar tarwatsa masu tada kayar baya.

Sama da shekaru hudu da barkewar yakin basasa a Syria amma har yanzu rikici na ci gaba da ruruwa.

A makon da ya gabata ne aka sake dage zaman sulhu da aka shirya yi bisa dalilai na kasa samun hadin kai tsakanin bangarorin da ke rikici da juna.

 

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.