Isa ga babban shafi
Yemen

MSF ta la’anci harin da aka kai a wata asibiti a Yemen

Kungiyar Agaji ta Medicins Sans Frontier ta yi allawadai da harin da aka kai wani asibiti a kasar Yemen wanda ya hallaka mutane 4.

Saudiya na ci gaba da kai hare hare ta sama kan mayakan huthi a Yemen
Saudiya na ci gaba da kai hare hare ta sama kan mayakan huthi a Yemen REUTERS/Abduljabbar Zeyad
Talla

Sanarwar da kungiyar ta bayar ta ce mutane 4 suka mutu sannan wasu 10 suka jikkata sakamakon harin da aka kai da makami mai linzami.

Kungiyar tace an kai harin ne a asibitin da k karkashin kulawarta a Razeh da ke Yankin Saada, kuma tuni aka kwashe ma’aikatan da ke ciki da masu jinya zuwa wasu asibitocin don kula da su.

Daraktan kungiyar Raguel Ayora ya ce ya zuwa yanzu ba za su iya cewar ko harin da Saudi Arabia ke kai wa ne ya samu asibitin ba ko kuma ‘yan tawaye ne suka harba makamin roka.

Jami’in ya ce akai-akai suna sanar da bangarorin da ke rikici a kasar ayyukan agajin da suke yi don ceto rayukan jama’a.

Saudiya da kawayenta dai na ci gaba da kai farmaki ta sama akan mayakan Huthi ‘Yan Shi’a da ke fada da gwamnatin Yemen.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.