Taliban
An gwabza fada tsakanin mayakan Taliban
An samu barkewar rikici tsakanin bangarorin kungiyar mayakan Taliban da ke gaba da juna a kudancin lardin Zabul a kasar Afghanistan. Mayakan da dama ne aka ruwaito sun mutu a rikicin da ya barke tsakanin masu biyayya ga Mullah Akhtar Mansour da kuma mabiyan Mansoor Dadullah.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahotanni sun ce tun a jiya mayakan ke kisan junansu inda aka kashe mutane kusan 100.
Jami’an tsaron Afghanistan sun ce tun a ranar Assabar ne rikicin ya barke, kuma rikicin ya sa an tsinci gawarwakin mutanen kabilar Hazaras da mayakan suka sace a watan Oktoba.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu