Isa ga babban shafi
Isra'ila

Sabon rikici ya barke a Masallacin birnin Kudus

Sabon rikici ya barke tsakanin Falasdinawa da Jami’an tsaron Isra’ila a safiyar yau litinin a harabar masallacin birnin Kudus.

Lokacin da Yan Sandan Isra'ila ke arangama da Falasdinawa a Masallacin birnin Kudus.
Lokacin da Yan Sandan Isra'ila ke arangama da Falasdinawa a Masallacin birnin Kudus. REUTERS/Ammar Awad
Talla

Jami’an ‘Yan Sanda sun yi ta wurga barkonon tsohuwa yayin da matasan Falasdinawa da suka yi alkawarin kare Masallacin na Kudus, suka yi ta wurga duwatsu.

Rohotanni sun ce, jim kadan da fara rikicin, ‘Yan Sanda sun tursasa wa Musulman da suka yi sallar asuba a Masallaci fice wa daga cikinsa yayin da kuma aka rufe dukkanin kofofin da Musumai ke bi domin shiga cikin Masallacin.

Tuni dai Hukumomin Isra’ila suka baza dimbin jami’an tsaro a gabashin birnin na Kudus har zuwa zagayen masallacin a daidai lokacin da yahudawa ke shirin gudanar da bukukuwan sallarsu ta shekara shekara mai suna Sukkot.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.