An kashe magoya bayan Al-Nosra 25 a yankin Idlib na Syria
Rahotanni daga Syria, na cewa magoya bayan kungiyar Al Nusra, reshen Alqa’ida da ke kasar su akalla 25 ne suka rasa rayukansu sakamokon fashewar bam a wani masallaci da ke birnin Ariha na lardin Idlib.
Wallafawa ranar:
Rami Abdel Rahman shugaban Kungiyar da ke sa ido kan abubuwan da ke faruwa a Syria, ya ce mai yiyuwa ne adadin wadanda suka rasa rayukansu ya zarta hakan, domin kuwa akwai wasu da dama da suka sami munanan raunuka sakamakon wannan fashewa.
Lamarin dai ya faru ne a daidai lokacin da daruruwan mutane suka taru a masallaci domin buda bakin azumin ranar jiya juma’a.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu