Isa ga babban shafi
Isra'ila

Ramadan: Dubban Musulmai sun yi sallar Jumma'a a birnin Kudus

Dubban musulmai ne suka gudanar da sallar Jumma’a a masallacin Baitul Mukaddis bayan sassauta matakan shiga masallacin da Isra ‘ila ta yi a yau albarkacin watan Ramadan.

Birnin Kudus
Birnin Kudus DR
Talla

Jami’an ‘yan sanda sun ce, kimanin musulamai dubu 80 ne daga birnin Kudus da yammacin kogin Jordan kadai suka halarci masallacin.

A bangare guda, Sheik Azzam Al-Khatib, Shugaban kwaminitin musulmai deke kula da masallacin ya shaidawa kamfanin dillacin labaran Faransa na AFP cewa, a kiyasce, masallata dubu 200 ne suka taru  a ciki da kewayen masallacin.

Kafin wannan ranar ta jumm’ar farkon Ramadan, ba kasafai ake barin musulmai shiga masallacin ba musamman matasa 'yan kasa da shekaru 40 saboda gudun tayar da tarzoma.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.