Hukumomin Myanmar sun sanar da ceto bakin haure
Yau juma'a sojan ruwan kasar Myanmar suka ce an ceto wasu mutanen da suka makale a kan teku, inda zuwa yanzu aka kawo mutane 208 zuwa kan tudu.Wannan na zuwa ne bayan da kasashen duniya suka ci gaba da yin matsin lamba ga kasar, na neman hanyoyin kawo karshen matsalar kwararar bakin haure zuwa kasashen Turai.
Wallafawa ranar:
Wani jami’an gwamnatin kasar, mai suna Tin Maung Swe ya sheida wa kamfanin dillacin labarun Faransa na AFP cewa zuwa yanzu an samo kwale kwale 2 kenan.
Sai dai hukumomin kasashen yankin za su mayar da hankali domin dakile kwararar bakin haure zuwa Turai,a cewar wani rahoto da suka futar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu