Isa ga babban shafi
Isra'ila

Isra’ila zata gina sabbin gidaje a yankunan Falesdinawa

Kasar Isra’ila tace tana shirin gina sabbin gidaje 1,500, domin mayar da martani ga gwamnatin Falesdinawa da ta hada kawance da Hamas. Shugabannin Falesidinawa sun yi kira ga Amurka ta dauki mataki akan Isra’ila.

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu
Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu REUTERS/Gali Tibbon
Talla

Isra’ila zata gina sabbin gidajen ne a yankunan Falesdinawa da ta mamaye a gabacin birnin Kudus da kuma yamma da kogin Jordan.

Ma’aikatar gidaje a kasar Isra’ila tace wannan martani ne akan kawancen da gwamnatin Falesdinawa ta kulla da Hamas, duk da kasashen yammaci da Amurka sun amince su yi aiki tare da sabuwar gwamnatin Hadin kan ta Falasdinawa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.