Isa ga babban shafi
Bangladesh

Abudlkader Mullah zai fuskanci hukunci kisa a Bangladesh

Kotun kolin kasar Bangladesh, a yau alhamis ta tabbatar da hukuncin kisan da wata kotun ta yankewa daya daga cikin shugabannin jam’iyyar Jama’ati Islami Abudlkader Mullah, saboda samun sa da laifin kashe jama’a a lokacin gwagwarmayar samawa kasar ‘yanci a shekarar 1971.

Abdul Kader Mullah Babban Shugaban Jam'iyyar 'Yan Uwa musulmi a Bangladesh
Abdul Kader Mullah Babban Shugaban Jam'iyyar 'Yan Uwa musulmi a Bangladesh Reuters
Talla

Mullah ya shigar da kara ne a gaban kotun kolin inda ya ke neman a soke umurnin zartas ma sa da hukuncin kisa ta hanyar ratayewa da wata kotun ta yanke masa a can baya.

A watan Fabrairu ne kotu ta yanke hukuncin samun Mullah da laifin aikata laifukan yaki a lokacin neman ‘Yanci daga Pakistan.

Tuni Mullah daya daga cikin shugabannin Jam’iyyar ‘Yan uwa Musulmi ya musanta zargin da ake masa.

Akwai shugabannin Jam’iyyar da dama da aka yanke wa hukunci, al’amarin da ya haifar da zanga-zanga daga magoya bayan Jam’iyyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.