Isa ga babban shafi
Bangladesh

Kotu ta yanke hukuncin kisa kan sojoji 150 a kasar Bangladesh

Babban mai shigar da kara na gwamnatin kasar ta Bangladeshe Baharul Islam, ya ce ko shakka babu wadannan sojoji 150, na da hannu dumu-dumu wajen kashe manyan jami’an sojan kasar a lokacin wannan bore.

Firayi ministar Bangladesh Sheikh Hasina
Firayi ministar Bangladesh Sheikh Hasina Unctad/Wikimedia Commons
Talla

A jimilce dai sojoji 350 ne kotun ta sama da laifi daga cikin 823 da aka gurfanar a gabanta, kuma an yanke masu hukuncin dauri da ya kama daga shekaru 4 zuwa 14 a gidan yari.

Masu boren dai sun balle rumbun ajiye makamai sannan suka dauke bindigogi dubu 2 da 500, kafin daga bisani su afka wa wani gini da manyan jami’an sojan kasar ke gudanar da taro, inda a can ne suka kashe 57 daga cikinsu bayan sun dan yi garkuwa da su na gajeren lokaci a ranar 25 ga watan fabarairun 2009 suna neman a kara masu albashi.
 

Har ila yau bayan sun kashe mutanen, masu bore sun jefa gawarwakinsu a cikin ramuka da kuma magudanan ruwa. Wannan ne dai boren soja mafi muni da kasar ta taba fuskanta a cikin tarihinta.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.