An kashe wasu 'yan gwagwarmayar yankin Kashemir su biyu
Rahotanni daga kasar India na nuna cewa ‘Yan kasar sun harbe wasu da ake zargin masu tsatsauran kishin Islama ne su biyu a yankin Pulwama da ke Kashmir, kana wasu fararen hula bakwai suka sami raunuka a lokacin da suke boren kashe mutanen biyu da aka yi.
Wallafawa ranar:
A cewar Mataimakin ‘yan sanda Vijay Kumar, mutanen biyun da aka kashe na da hanu a wani harin bam da aka kai wanda ya yi sanadiyyar mutuwar wasu mata hudu ‘Yan yawon bude ido a yankin na Kashmir.
Ya kara da cewa, a yanzu haka an saka dokar hana fita a yankin.
Kasar India dai na zargin kasar Pakistan da marawa masu tsatsauran ra’ayin kishin Islama baya, inda suke kai munanan hare-hare a yankin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu