Babban mai shigar da kara a Korea ta Kudu ya yi murabus
A yau Juma’a, Babban mai gabatar da kara na kasar Koriya ta kudu, ya yi murabus, tare da neman afuwar ‘Yan kasar, saboda sakamakon wasu lamuran abin kunyan da suka shafi bangare shari’an kasar.
Wallafawa ranar:
Lokacin da yake bayyana murabus din nashi, Han Sang-Dae, ya bayyana nadama kan badakalar da ta shafi wani babban mai gabatar da kara daya karbi cin hanci, da wani da ban daya nemi yin lalata, da mace don yin sassauci a hukunci.
Badakalar bangaren shari’ar kasar, ta zafafa takun sakan da ke tsakanin Han, da wani abokin hamayyar shi, da ke jagorantar sashen da ke bincike kan ma’aikata masu aikata almundahana a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu