Isa ga babban shafi

Majalisar Sojin Mali ta kawo karshen yarjejeniyar Algiers da aka rattabawa hannu a 2015 da Abzinawa

A kasar Mali,majalisar soji ta sanar da kawo karshen  tare da aiwatar da matakin nan take na yarjejeniyar Algiers da aka rattabawa hannu a shekarar 2015 da kungiyoyin Abzinawa masu neman 'yancin kai a arewacin kasar.

Wasu daga cikin yan tawayen Abzinan arewacin Mali
Wasu daga cikin yan tawayen Abzinan arewacin Mali REUTERS/Adama Diarra/Files
Talla

A cikin sanarwa da suka fitar zuwa manema labarai , Mali ta bayyana abin rashin jin daɗi,ganin rawar da makwabciyarta Aljeriya ke takawa a bangaren da ya shafi Hulda da sanin abinda ya dace tsakanin kasashen biyu.

Birnin Gao na kasar Mali
Birnin Gao na kasar Mali © Souleymane AG ANARA / AFP

Yarjejeniyar zaman lafiyar da aka sanya hannu a shekarar 2015 tsakanin kasar Mali da kungiyoyin 'yan tawaye, ta kasance marar tushe, in ji sanarwar da aka fitar wacce ke nuna karshenta a hukumance.

Don tabbatar da wannan matsayi, gwamnatin soji ta nuna damuwa  ganin rawar da wasu kungiyoyin Abzinawa ke takawa tare da canza salo a fuskoki da dama.

Shugaban Majalisar Sojin Mali Kanal  Assimi Goïta.
Shugaban Majalisar Sojin Mali Kanal Assimi Goïta. © ORTM

Majalisar Soji ta yi tir da wasu daga cikin manufofi na nuna kyama da cin zarafi daga hukumomin na Algeria.

Hukumomin Mali na danganta kungiyoyin Abzinawa da suka bijerewa dokokin kasar ta Mali a matsayin yan ta'adda".

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.