Isa ga babban shafi

EU ta jaddada goyon bayanta ga Jakadan Faransa da ke killace a Nijar

Tarayyar Turai ta, ta bakin jagoran diflomasiyyarta, Josep Borrell  ta  bayyana goyon bayanta ga jakadan Faransa a Jamhuriyar Nijar, Sylvain Itte, wanda ke fuskantar matsanancin matsin lamba bayan da ya ki bin umurnin da aka ba shi na ficewa daga kasar.

Jagoran diflomasiyyar Kungiyar Tarayyar Turai EU, Josep Borrell
Jagoran diflomasiyyar Kungiyar Tarayyar Turai EU, Josep Borrell AP
Talla

Tarayyar Turai ta kuma sabanta goyon bayanta ga Mohamed Bazoum, zababben shugaban Jamhuriyar Nijar da aka hambarar, wanda ke tsare a halin yanzu, tana mai yabawa da jajircewarsa.

Yaki da ta'addanci a Sahel

Borrell ya  kuma ce kungiyar Turai ta amince da bukatar sake salo a yakin da ake da ta’addanci a yankin Sahel, wanda Faransa ta jagoranta tsawon shekaru.

A  makon da ya gabata, shugaba Emanuel Macron ya  ce  sojojin da suka yi juyin mulki sun yi garkuwa da jakadan a ofishin jakadancin kasar da ke birnin Yamai, inda suke ciyar da shi abincin da sojoji ke ci ,bayan da suka hana a sshigo masa da nasa abincin.

Jagoran diflomasiyyar EU, Josep Borrell da Franministan Nijar Hasoumi Masaoudi.
Jagoran diflomasiyyar EU, Josep Borrell da Franministan Nijar Hasoumi Masaoudi. AP - Andrea Comas

Bayan kifar da gwamnatin Bazoum Mohamed a watan Yuli, sojojin da suka yi wannan aiki sun fusata da yadda tsohuwar uwargijiyar  tasu ta ta nuna rashin amincewa da gwamnatinsu, lamarin da ya sa suka kori jakadan Faransa a kasar, 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.