Isa ga babban shafi

Wasu masu dauke da makamai sun karbe sansanonin soji 2 arewacin Mali

Wasu mutane dauke da makamai sun kame wani sansanin soji a arewacin Mali a jiya Lahadi, kamar yadda wasu jami’an gwamnatin kasar suka tabbatar,  bayan da kungiyar ‘yan  tawayen Azbinawa   ta  dau alhakin harin.  

Taswirar kasar Mali da ke nuna yankin Timbuktu..
Taswirar kasar Mali da ke nuna yankin Timbuktu.. © FMM
Talla

 

A jiya Lahadi rundunar sojin Mali ta  tabbatar da aukuwar lamarin a dandalin sada zumunta, inda ta ce da misalin karfe 3 da rabi agogon GMT ne maharan suka afka wa garin Lere da ke yankin Timbuktu na arewacin kasar.  

Wata  majiya ta ce bayan ba-ta-kashi ne maharan suka kwace sansanin, kuma a halin da ake ciki yana hannunsu. 

Wani jami’in gwamnatin yankin ya ce an samu asarar rayuka, said dai har yanzu ba a kai ga tantance adadin wadanda suka mutu ba. 

A shekarar 2012 ce ‘yan tawaye Azbinawa masu neman ballewa daga kasar suka kaddamar da hare-hare, kafin daga bisai suka rattaba hannu a yarjejeniyar zaman da gwamnatin kasar a shekarar 2015; sai dai yarjejeniyar na daf da wargajewa. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.