Isa ga babban shafi

Annobar cutar cholera ta kashe mutane 426 a Kamaru

Ma’aikatar lafiyar Kamaru ta tabbatar da yadda annobar cutar Cholera ta kashe mutanen da yawansu ya haura 400 daga lokacin barkewar cutar zuwa yanzu.

Baya ga Kamaru kasashen Mozambique da Malawi na sahun wadanda ke ganin tsanantar annobar cutar ta kwalara ko kuma amai da gudawa.
Baya ga Kamaru kasashen Mozambique da Malawi na sahun wadanda ke ganin tsanantar annobar cutar ta kwalara ko kuma amai da gudawa. AFP - MAURICIO FERRETTI
Talla

Bayan karuwar mutanen da cutar ta kashe a makwanni biyu da suka gabata da adadin mutane 26 alkaluman wadanda suka mutu sanadiyyar annobar ta Cholera a sassan kamaru ya karu zuwa mutum 426.

Tun a watan Oktoban shekarar 2021 ne Kamaru ta fara ganin annobar cutar ta Cholera amma kuma a watan Maris din shekarar nan ne cutar ta matukar tsananta inda yanzu haka mutane dubu 1 da 868 ke jinya bayan kamuwa da cutar.

Hukumar lafiya ta Duniya WHO ta yi gargadin cewa, cutar ta zarta lokacin da bisa al’ada ta kanyi tafiyar hawainiya gabanin yaduwa, Wanda ken una bukatar daukar matakan gaggawa don dakile ci gaba da yaduwarta.

WHO ta ce barkewar cutar a wannan lokacin babban abin fargaba ne, kasancewar ana ci gaba da samun bullarta a kasashen makwabta.

Mahukuntan Lafiyar Kamaru sun ce kashi 79 cikin dari na wadanda suka kamu da cutar sun samu kulawar lafiya dalilin da ya taimaka wajen dakile yaduwarta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.