Isa ga babban shafi

Yakin Sudan ya raba sama da mutane dubu 400 da gidajensu

Majalisar Dinkin Duniya ta ce sama da mutane dubu dari 3 da 30 ne rikicin Sudan ya sanya su barin gidajen su, inda kuma wasu sama da dubu dari suka bar kasar. 

Wasu mazauna Sudan yayin kokarin ficewa daga kasar don gujewa fadan da ake gwabzawa tsakanin rundunonin dakarun kasar biyu.
Wasu mazauna Sudan yayin kokarin ficewa daga kasar don gujewa fadan da ake gwabzawa tsakanin rundunonin dakarun kasar biyu. REUTERS - EL TAYEB SIDDIG
Talla

Hukumar Kula da ‘Yan Cirani na Majalisar ta yi kiyasin cewa, kimanin mutane dubu dari 3 da 34 ne ke gudun hijira a cikin kasar tun bayan barkewar rikicin a ranar 15 ga watan Afrilun da ya gabata. 

Adadin mutanen da suka yi gudun hijira a cikin makwanni biyu da fara rikicin, ya zarce adadin gaba daya wadanda suka yi gudun hijira a rikicin kasar na shekarar 2022. 

Har wayau, Kakakin Hukumar Bada Agaji na Majalisar Jens Laerke ya ce kashi 14 ne kadai aka samu na yawan gudunmuwar da ake bukata a gidauniyar bada agaji ta kasar da aka samar a wannan shekarar, inda a yanzu akwai gibin kusan dalar Amurka biliyan daya da miliyan dari biyar. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.