Isa ga babban shafi

Kamala Harris ta isa Ghana a ziyarar kasashen Afrika 3 da ta faro

Mataimakiyar Shugaban Amurka Kamala Harris ta isa birnin Accra na kasar Ghana a yammacin yau lahadi, zangon farko a ziyarar da za ta gudanar cikin kasashe uku na nahiyar Afirka. 

Mataimakiyar shugaban kasar Amurka Kamala Harris bayan isar ta birnin Accra na Ghana yau lahadi 26 ga watan Maris na shekarar 2023.
Mataimakiyar shugaban kasar Amurka Kamala Harris bayan isar ta birnin Accra na Ghana yau lahadi 26 ga watan Maris na shekarar 2023. AP - Misper Apawu
Talla

Baya ga kasar ta Ghana, Harris za ta ziyarci Tanzania da kuma Zambia, inda a kasar Ghana, za ta tattauna da shugaba Nana Akufo-Addo da kuma shugabannin wasu kungiyoyin fararen hula na kasar. 

Yayin da a Ghana Harris ke shirin karfafa gwiwar kungiyoyin fararen hula tare da shawarwari ga gwamnatin kasar game da halin matsin tattalin arzikin da kasar ke fama da su, can a Tanzania kuwa mataimakiyar shugaban na Amurka za ta tabo batun 'yanci da kuma baiwa mata damarmakin shiga a dama da su a lamurran kasar.

Wannan ziyara dai na zuwa ne a dai dai lokacin da Amurka ke kokarin janyo kasashen Afrika cikinta bayan da Rasha ke kokarin zabe musu uwar gijiya sakamakon yadda ta ke karfafa ikonta ta fuskar karfin soji a nahiyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.