Isa ga babban shafi

Tanzania: Sama da kashi 90 na daliban nazarin aikin lauya ne suka fadi jarabawa

Lauyoyi a kasar Tanzaniya sun nuna damuwa bayan rahotannin da ke cewa dalibai 26 ne kawai daga cikin 633 ne suka samu nasarar cin jarabawa a kwalejin nazarin aikin lauya, wanda ke nuna adadin da kashi 4.1 cikin dari.

Masu ruwa da tsaki a bangaren shari'a na danganta wannan matsala da rashin mayar da hankali kan jami'o'in kasar.
Masu ruwa da tsaki a bangaren shari'a na danganta wannan matsala da rashin mayar da hankali kan jami'o'in kasar. © AFP
Talla

Jaridar Mwananchi ta ruwaito cewa dalibai 342 ne aka yi hasashen za su samu nasara a jarrabawar, yayin da wasu 265 aka dakatar da su baki daya.

Wadanda suka kammala karatu daga jami’o’i daban-daban sai sun ci jarrabawar a kwalejin nazarin aikin lauya kafin a rantsar da su a matsayin lauyoyi.

An dora alhakin rashin nasarar daliban da aka samu dai a kan rashin inganta harkokin jami'o'in kasar, kamar yadda mahukuntan kwalejojin shari'a suka ruwaito.

Ko a shekarun da dama da suka gabata ma an samu raguwar nasarar dalibai, amma sakamakon bana ya kasance mafi muni a cikin ‘yan shekarun nan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.