Isa ga babban shafi

Gwamnatin Benin ta kwace illahirin kadarorin dan adawa Sebastien Ajavon

Gwamnatin Jamhuriyar Benin ta kwace illahirin kadarorin jagoran ‘yan adawar kasar Sebastien Adjavon da ke gudun hijira a Faransa, bayan da kotu ta same da laifin kin biyan harajin da ya kai cfa milyan 160.

Sebastien Ajavon, jagoran yan adawa na Jamhuriyar Benin
Sebastien Ajavon, jagoran yan adawa na Jamhuriyar Benin REUTERS
Talla

A ranar 22 ga watan maris da ya gabata ne kotun koli ta tabbatar da samun dan adawar da wannan laifi, inda a karshen mako wakilin kotu da kuma jami’an tsaro suka shiga gidansa da ke birnin Kwatanu tare da kwashe illahirin kadarorinsu.

Lauyan jagoran yan adawan Jamhuriyar Benin Me Marc Bensimon ya bayyana takaicin sa ganin ta yada gwamantin kasar ta Benin ke yiwa jagoran yan adawa bita da kuli.

Tun a shekara ta 2017 ne Jagoran yan adawar kasar ta Benin,Sebastien Ajavon ke samu mafaka a Faransa.

Yan adawa na kalon Shugaban kasar Patrice Talon a matsayin dan kama karya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.