Isa ga babban shafi

Majalisar sojin Burkina Faso ta kasa magance hare-haren yan ta'adda

Dakarun Burkina Faso 11 ne suka rasa rayukan su biyo bayan wani  harin mayakan jihadi a jiya alhamis  a gabashin kasar. Majalisar sojin kasar na iya kokarin shawo kan wannan matsalar mayakan jihadi a Burkina Faso.

Jami'an tsaron kasar Burkina Faso
Jami'an tsaron kasar Burkina Faso © AFP
Talla

A dan tsakanin nan kasar ta Burkina Faso ta fuskanci hare-haren mayakan jihadi, al’amarin dake neman durkusar da sha’anin tsaro ga baki daya a wannan yanki.

Rashin tsaro na daga cikin matasalolin da suka yi awon gaba da tsofuwar gwamnatin tsohon Shugaban kasar Christian Kabore da aka yiwa juyin mulki,duk da kokarin kungiyar G5 Sahel a lokacin.

Rashin kayan aiki da horo da ya dace suka  tilastawa majalisar sojin kasar sake gayyato tsofin sojojin kasar a wannan yaki da yan ta’adda.

Abba Seidk masanin harakokin siyasa da zamantakewar kasashen yammacin Afrika ya bayyana yada yake kalon wannan al’amari.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.