Majalisar sojin Burkina Faso ta kasa magance hare-haren yan ta'adda
Dakarun Burkina Faso 11 ne suka rasa rayukan su biyo bayan wani harin mayakan jihadi a jiya alhamis a gabashin kasar. Majalisar sojin kasar na iya kokarin shawo kan wannan matsalar mayakan jihadi a Burkina Faso.
Wallafawa ranar:
Kunna - 01:04
A dan tsakanin nan kasar ta Burkina Faso ta fuskanci hare-haren mayakan jihadi, al’amarin dake neman durkusar da sha’anin tsaro ga baki daya a wannan yanki.
Rashin tsaro na daga cikin matasalolin da suka yi awon gaba da tsofuwar gwamnatin tsohon Shugaban kasar Christian Kabore da aka yiwa juyin mulki,duk da kokarin kungiyar G5 Sahel a lokacin.
Rashin kayan aiki da horo da ya dace suka tilastawa majalisar sojin kasar sake gayyato tsofin sojojin kasar a wannan yaki da yan ta’adda.
Abba Seidk masanin harakokin siyasa da zamantakewar kasashen yammacin Afrika ya bayyana yada yake kalon wannan al’amari.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu