Isa ga babban shafi
Burkina-Ta'addanci

'Yan bindiga sun tseratar da fursinoni 60 a farmakin gidan yarin Burkina Faso

‘Yan bindiga sun sako fursunoni kusan 60 a wani hari da suka kai wani gidan yari a arewa maso yammacin kasar Burkina Faso cikin dare, tare da kona motoci kafin su tsere.

Matsalar tsaro na ci gaba da ta'azzara a sassan Burkina Faso.
Matsalar tsaro na ci gaba da ta'azzara a sassan Burkina Faso. © RFI
Talla

Sanarwar da hukumomin tsaron kasar suka fitar ta ce mutanen dauke da makamai sun shiga garin Nouna ne da tsakar dare a kan motoci  da kuma babura, inda suka yi ta harbin kan mai ‘uwa dawabi.

Burkina Faso dai na fama da hare-haren masu jihadi da suka yadu daga makwabciyarta Mali cikin shekaru goma da suka gabata, inda ake kai munanan hare-hare a duk mako.

Abin da bayanai ke cewa shine, an kashe dubban mutane a fadin kasar, kuma an tilasta wa miliyoyin jama’a kauracewa gidajensu, sakamakon hare-haren masu tayar da kayar baya.

Babu wanda ya rasa ransa a harin da aka kai gidan yarin, amma an harbe wani mayakin sa kai a cewar majiyoyin tsaro. An kuma kona motoci da babura da dama, baya ga yin barna a ofisoshin gidan yarin.

Har yanzu dai babu wata kungiya da ta dauki alhakin kai harin.

Wannan farmakin ya zo ne sa’o’i kadan bayan wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe akalla mutane 11 a tsakanin garuruwan Dori da Gorgadji da ke arewacin kasar, kuma daga cikin wadanda suka mutu har da 'yan bindiga 9 da fararen hula biyu.

Rundunar sojin Burkina Faso a ranar Juma'a ta ce an kashe wasu sojoji 11 da 'yan bindiga da kuma jami'an 'yan sanda a wasu hare-haren da aka kai a cikin makon da ya gabata, amma sama da 'yan ta'adda 20 ne aka kashe a wani ramuwar gayya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.