Isa ga babban shafi

Gobara ta lakume gidaje da dama a Afrika ta tsakiya

Kusan mutane dubu biyar suka rasa muhallansu a Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya bayan gobara ta cinye sansaninsu kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana.

Al'umar kasar Afrika ta Tsakiya
Al'umar kasar Afrika ta Tsakiya © Club RFI Bangui Fononon
Talla

Jumullar mutane dubu 4 da 802 ne ke bukatar mazauni cikin gaggawa da kuma abinci da ruwan sha har ma da kayayyakin masarufi a Jamhuriyar Tsakiyar Afrika kamar yadda Anita Cadonau, jami’ar yada labaran ofishin Majalisar Dinkin Duniya mai kula da jinkai ta sanar.

A ranar Talatar da ta gabata, aka samu ibtila’in gobarar a sansanin Alindao mai tazarar kilomita 500 daga gabashin birnin Bangui.

Mutane 20 ne aka bada rahoton cewa, sun jikkata sakamakon ibtila’in.

Gobarar ta tashi ne bayan wani karamin yaro ya yi kokarin yin girki da man-ja a cewar daya daga cikin wadanda suka shaida lamarin.

Gobara a wani yankin Afrika
Gobara a wani yankin Afrika AFP - HANDOUT

Jamhuriyaar Afrika ta Tsakiya dai na cikin kasashen duniya mafi fama da bakin-talauci, yayin da ta fama cikin yakin-basasa a shekara ta 2013 bayan kifar da gwamnatin  shugaban kasar na wancan lokacin, Francois Bozize.

Wannan juyin mulkin da ‘yan tawaye suka yi masa, ya haddasa zubar da jini tsakanin dakarun Seleka na Musulmai  da kuma Anti-Balaka  na Kiristoci.

Faransa da Majalisar Dinkin Duniya ne suka yi uwa-suka-yi makarbiya wajen maido da zaman lafiya a kasar a wancan lokacin, inda har aka gudanar da zaben shugaban kasa. Kodayake har hanzu, ‘yan tawaye na ci gaba da rike da yankuna da dama na kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.