Isa ga babban shafi
Faransa - Burkina Faso

An harbe mutane 4 yayin zanga-zangar kin jinin sojojin Faransa a Burkina Faso

Wasu majiyoyi daga kasar Burkina Faso suka ce akalla mutane hudu suka samu rauni, bayan da dakarun kasar da na Faransa suka bude wuta a kokarin dakile masu zanga-zangar da ke kokarin toshe ayarin motocin sojojin Faransa.

Jerin gwanon motocin sojin Faransa a Burkina Faso.
Jerin gwanon motocin sojin Faransa a Burkina Faso. © MICHELE CATTANI / AFP
Talla

Wata majiya a garin Kaya da ke arewacin babban birnin kasar ta ce masu zanga-zangar sun yi kokarin tunkarar jami'an sojojin Faransa a wani yanki da suka shafe dare.

Majiyar lafiya ta ce "ma'aikatar gaggawa ta asibitin Kaya ta karbi mutane hudu da suka samu raunukan harbin bindiga".

Sai dai wata majiyar sojan Faransa ta musanta cewa an jikkata mutane,  inda ta yi watsi da alhakin abin da ya wakana.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.