Isa ga babban shafi
Benin - Faransa

Kasar Benin ta karbi kadarorin sarauta kusan 30 da Faransa ta kwace mata

Gwamnatin Benin a ranar Laraba 10 ga watan Nuwamba ta yi maraba da kadarorin sarauta kusan 30 da aka wawashe daga kasar dake yankin Afirka ta yamma a lokacin mulkin mallakar turawan Faransa fiye da shekaru 130 da suka gabata.

Shugaban Faransa Emmanuel Macron yayin duba kofofin fadar Sarki Glele na karni na 19 a jamhuriyar Benin a gidan kayan tarihi na Quai Branly da ke Paris, babban birnin kasar Faransa, Oktoba 27, 2021.
Shugaban Faransa Emmanuel Macron yayin duba kofofin fadar Sarki Glele na karni na 19 a jamhuriyar Benin a gidan kayan tarihi na Quai Branly da ke Paris, babban birnin kasar Faransa, Oktoba 27, 2021. © Michel Euler/Pool via REUTERS
Talla

Shugaban kasar Benin Patrice Talon da ministan al'adu na kasar sun yi tattaki a ranar Talata zuwa birnin Paris domin karbo kayayyakin tarihi guda 26.

Jirgin dake dauke da dukiyar masarautar ya sauka ne da yammacin Laraba a filin jirgin saman Cotonou, inda daruruwan mutane suka taru don nuna girmamawa, da kuma bayyana farin cikinsu.

A karshen watan Oktoba katafaren gidan adana kayan tarihi Quai Branly dake birnin Paris yayi baje-kolin gwamman kayayyakin tarihi da dakarun Faransa suka kwaso daga kasar Benin a zamanin mulkin mallaka, wanda kuma ya zama karo na karshe da za a nuna kayayyakin tarihin a Faransa kafin a mayar da su ga kasar ta Benin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.