Isa ga babban shafi
Mali - ECOWAS

'Yan Mali sun yi zanga-zangar neman karawa sojoji wa'adin mulki

Daruruwan mutane sun yi zanga -zanga a Bamako babban birnin Mali, inda suka bukaci a ba wa shugabannin sojan kasar karin lokaci don tsara zaben da zai sake mayar da mulki ga farar hula.

'Yan kasar Mali yayin murnar juyin mulkin da sojoji suka yi a birnin Bamako.
'Yan kasar Mali yayin murnar juyin mulkin da sojoji suka yi a birnin Bamako. © MALIK KONATE / AFP VIA GETTY IMAGES
Talla

Zanga-zangar ta zo ne bayan da a ranar Alhamis, kungiyar kasashen Afirka ta Yamma ECOWAS ta ce ba za a sauya jadawalin mika wa farar hula mulki a watan Fabarairu ba.

Bayan juyin mulkin da sojoji suka yi wa tsohon shugaban Mali Ibrahim Boubacar Keita a watan Agustan shekarar 2020, sun nada gwamnatin farar hula ta wucin gadi da aka dorawa alhakin mayar da kasar kan mulkin dimokaradiyya.

Sai dai a watan Mayu sojojin a karkashin Kanal Assimi Goita suka sake kwace mulki gami da ayyana shi a matsayin shugaban rikon kwarya.

Goita ya yi alkawarin mutunta wa'adin na shirya zaben na watan Fabrairu, to amma wasu na shakku game da hakan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.